DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An tura wa jihohi 36 da Abuja naira Tiriliyan 1.6 cikin watanni 15 -Gwamnatin Tarayya

-

Daga watan Maris 2024 zuwa Mayun 2025, gwamnatin tarayya ta raba Naira tiriliyan 1.6 ga jihohi 36 da babban birnin tarayya (FCT) domin ayyukan more rayuwa da tsaro.

Wannan na kunshe ne a cikin wani rahoto daga Ofishin Akanta Janar na Tarayya (OAGF), da aka mika wa kwamitin rabon kudin tarayya a watan Mayun 2025 don inganta tsaro da habbaka ilimi da lafiya a jihohin.

Google search engine

Jaridar Punch ta ruwaito cewa an fito da kudin ne daga ajiyar kudaden shiga da ba na bangaren mai ba, karkashin shirin tallafin gaggawa da aka kafa bayan cire tallafin man fetur.

An fara rabon da N200bn a Maris 2024, yayin da aka ci gaba da raba kusan N100bn a kowane wata. Babban adadin da aka raba a wata guda shi ne N222bn a watan Mayun 2024.

Duk da wannan yawan kudi, rahoton bai fayyace yadda kowace jiha ta karɓi nata rabon ba. Sai dai Naira N1.7, da asusun ya tara an yi amfani da N1.6tn, ya rage N100bn a asusun.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon Minista Tanimu Turaki ya zama ɗan takarar shugabancin jam’iyyar PDP na Arewa

Jagororin jam’iyyar PDP na yankin Arewacin Nijeriya sun amince da tsohon Ministan Harkoki. A Musamman, Tanimu Turaki (SAN), a matsayin ɗan takarar da suka amince...

Jam’iyyar ADC a Kaduna ta kori mataimakin shugabanta da wasu ‘ya’yanta 8

Jam'iyyar hadaka ta ADC mai hamayya a Nijeriya reshen Kaduna ta kori mataimakin shugabanta na jihar tare da wasu manyan jami'anta guda takwas, bayan samun...

Mafi Shahara