DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hadimin Sanata Ipinsagba ya yi murabus saboda albashin N20,000 da ake biyansa

-

Oluwatunbosun Awe, mataimaki na musamman ga Sanata Olajide Ipinsagba mai wakiltar yankin Ondo Arewa a Majalisar Dattawa, ya yi murabus daga mukaminsa bisa albashin N20,000 da ake biyansa a kowane wata.

Awe, wanda ke matsayin jami’in hulɗa da mazabu a gundumar Isowopo Ward 2, karamar hukumar Akoko North East ta jihar Ondo, ya bayyana murabus dinsa a cikin wata wasika da aka fitar a ranar Laraba.

Google search engine

Ya ce albashin bai dace da halin tattalin arzikin Najeriya a yanzu ba, musamman duba da sabon albashin ƙasa na N70,000 da aka amince da shi kwanan nan.

Ya bayyana cewa duk da roƙon da ya yi wa Sanata Ipinsagba kan a duba albashinsa, ba a ɗauki wani mataki ba, kodadai makusantan sanatan sun yi watsi da dalilan murabus din nasa, kamar yadda Jaridar Daily Trust ta tabbatar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara