DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan Nijeriyar da ke zuwa kasashen waje na biyan harajin jirgi da tsada, in ji wani rahoto

-

Fasinjojin jiragen sama da ke tashi daga Nijeriya na biyan ɗaya daga cikin mafi tsadar haraji da kuɗaɗen jirgi a nahiyar Afirka, inda matsakaicin kuɗin da ake biya ga kowane fasinja a tafiyar ƙetare ya kai dala $180 — kusan sau uku na matsakaicin kuɗin nahiyar wanda yake dala $68, a cewar wani sabon rahoto daga Ƙungiyar Kamfanonin Jiragen Sama na Afirka (AFRAA).

Nazarin, mai take AFRAA Taxes and Charges Study Review 2024, wanda jaridar PUNCH ta samu, ya bayyana yadda yawan haraji da kuɗaɗe ke hana bunƙasar harkar sufurin jiragen sama a Afirka tare da ɗora wa matafiya nauyin da bai kamata ba.

Google search engine

Nijeriya na matsayi na uku cikin ƙasashen da ke da mafi tsadar haraji da kuɗaɗen tikitin jirgi a Afirka, tana bin bayan Gabon da Saliyo. Sauran ƙasashen Yammacin Afirka da suka shiga cikin jerin goma na ƙasashen da suka fi tsadar haraji a zirga-zirgar jiragen sama sun haɗa da Nijar, Benin, da Ghana.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara