Sabon shugaban jam’iyyar APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya bayyana cewa zai dauki wasu muhimman matakai masu tsari domin sake gina jam’iyyar da tabbatar da shugabanci nagari.
Da yake zantawa a shirin Politics Today na Channels TV, Yilwatda ya ce sabon jagorancinsa zai kasance mai gaskiya da tsauri, tare da bude kofa ga kowa, ciki har da jagoran tafiyar Kwankwasiyya, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, da duk wanda ke da sha’awar sauya sheka zuwa APC.
Farfesa Yilwatda ya kuma bayyana cewa a halin yanzu babu wata jam’iyya mai karfin da za ta iya karawa ko kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaben 2027, yana mai cewa APC na da cikakken tsari da goyon bayan jama’a don ci gaba da mulki.



