DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dangote ya yi ritaya daga matsayin shugaban kamfanin siminti na Dangote Cement

-

Attajirin Afirka, Alhaji Aliko Dangote, ya ajiye kujerarsa a matsayin shugaban hukumar gudanarwar kamfanin Dangote Cement Plc, daga ranar 25 ga Yuli, 2025.

Wata sanarwa da kakakin kamfanin, Anthony Chiejina, ya fitar, ta bayyana cewa Dangote zai mayar da hankali sosai kan matatar mai, masana’antar sinadarai, takin zamani da kuma hulda da gwamnati, domin kara hanzarta ci gaban kasuwancin kamfaninsa cikin shekaru biyar masu zuwa.

Google search engine

Biyo bayan hakan, kamfanin ya sanar da Emmanuel Ikazoboh a matsayin sabon Shugaban Hukumar Gudanarwar kamfanin.
Ikazoboh na daya daga cikin manyan daraktoci masu zaman kansu a hukumar.

Hakazalika, Mariya Aliko Dangote ta samu shiga cikin Hukumar Gudanarwar kamfanin, yayin da Farfesa Dorothy Ufot ta yi murabus.

Dangote Cement dai kamar yadda gidan talabijin na Channels ya ruwaito na daya daga cikin manyan kamfanonin masana’antu a nahiyar Afirka, kuma yana taka muhimmiyar rawa a ci gaban tattalin arzikin Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara