DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kashim Shettima ya wakilci Tinubu a taron majalisar dinkin duniya kan tsaron abinci a Habasha

-

Mataimakin shugaban ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya wakilci Shugaba Bola Ahmed Tinubu a taron koli na Majalisar Ɗinkin Duniya kan tsarin abinci (UNFSS+4) da aka gudanar a Addis Ababa, babban birnin ƙasar Habasha.

A jawabin da ya gabatar a madadin shugaban ƙasa, Shettima ya bayyana cewa taron na da nufin samar da makoma mai ɗorewa wadda ke ginuwa kan yalwa, daidaito da mutuncin ɗan’adam.

Google search engine

Ya ce Afirka na buƙatar tallafin kuɗi mai sauƙi kuma tabbatacce don zuba jari a harkar noma, inganta karkara, ilimi da ababen more rayuwa, tare da buƙatar daidaita kuɗaɗen sauyin yanayi da tsarin abinci.

Ya ƙara da cewa Najeriya na ƙara ƙaimi a bangaren noma ta amfani da fasahar zamani irin su Artificial Intelligence (AI), geospatial analytics, da bayanan tauraron dan adam domin magance ƙarancin abinci a ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara