DCL Hausa Radio
Kaitsaye

APC ta fara samun baraka a wasu jihohin Nijeriya in ji wani binciken jaridar Punch

-

Duk da cewa jam’iyyar APC na rike da iko a matakin tarayya da kuma jihohi 23, tana fuskantar mummunan rikici na cikin gida da ke kara ta’azzara.

Rikice-rikicen bangaranci, zargin ƙaƙaba shugabanci, da rashin warware matsalolin jagoranci sun fara kawo barazana ga hadin kan jam’iyyar yayin da ake shirin fuskantar babban zaben 2027.

A cewar jaridar Punch, yawancin reshen jam’iyyar da ke cikin rudani sun haɗa da Lagos, Rivers, Delta, Bayelsa, Benue da Akwa Ibom.

Google search engine

Wannan ya tilasta shugabannin jam’iyyar a matakin kasa shiga tsakani domin shawo kan rikicin da ke barazanar dagula tsarin mulki da tasirin siyasar jam’iyyar.

A baya-bayan nan, APC ta sha fama da rabuwar kai da rikicin shugabanci da ke barazana ga daidaituwarta, duk da karbar wasu fitattun ’yan adawa ciki har da wasu gwamnoni da suka sauya sheka zuwa jam’iyyar.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Jami’ar gwamnatin tarayya da ke Dutse a jihar Jigawa ta kori dalibai 20 tare da dakatar da wasu 15 bisa zarginsu da satar jarrabawa

Jami'ar tarayya da ke jihar Jigawa ta kori dalibai 20 tare da dakatar da wasu 15 daga karatu bisa samunsu da laifin satar jarabawa. Rahotanni sun...

Mafi Shahara