Duk da cewa jam’iyyar APC na rike da iko a matakin tarayya da kuma jihohi 23, tana fuskantar mummunan rikici na cikin gida da ke kara ta’azzara.
Rikice-rikicen bangaranci, zargin ƙaƙaba shugabanci, da rashin warware matsalolin jagoranci sun fara kawo barazana ga hadin kan jam’iyyar yayin da ake shirin fuskantar babban zaben 2027.
A cewar jaridar Punch, yawancin reshen jam’iyyar da ke cikin rudani sun haɗa da Lagos, Rivers, Delta, Bayelsa, Benue da Akwa Ibom.
Wannan ya tilasta shugabannin jam’iyyar a matakin kasa shiga tsakani domin shawo kan rikicin da ke barazanar dagula tsarin mulki da tasirin siyasar jam’iyyar.
A baya-bayan nan, APC ta sha fama da rabuwar kai da rikicin shugabanci da ke barazana ga daidaituwarta, duk da karbar wasu fitattun ’yan adawa ciki har da wasu gwamnoni da suka sauya sheka zuwa jam’iyyar.



