DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun sace mata 20 a wani sabon hari a jihar Zamfara

-

A kalla mata da ‘yan mata 20 ne ‘yan bindiga suka sace a garin Moriki da ke karamar hukumar Zurmi a jihar Zamfara, yayin da suke neman itace a wajen gari a ranar Asabar.

Wani mazaunin yankin, Sufyanu Moriki, ya tabbatar da faruwar lamarin ga gidan talabijin na Channels, yana mai cewa har yanzu masu garkuwar ba su nemi kudin fansa ba.

Google search engine

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara Yazid Abubakar ya ce hukumar su ba ta samu bayani kan lamarin ba tukuna.

Rahotanni sun bayyana cewa hadin gwiwar ‘yan ta’adda da mayaka ma su da’awar jihadi na kungiyar Lakurawa a yankin na kara dagula lamarin tsaro a Arewacin Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Manyan Jami’an soji za su fuskanci ritayar dole bayan sauye-sauye a fannin tsaron Nijeriya

Rahotanni sun tabbatar da cewa akwai manyan jami'an sojin Nijeriya  masu mukamin Janar akalla 60 da za su fuskanci ritayar dole, biyo bayan sauye-sauyen da...

Rashin gogewar siyasa ta sa ban tsayar da El-Rufa’i don ya gaje ni ba – Obasanjo

Tsohon shugaban Nijeriya Olusegun Obasanjo ya bayyana cewa ya ki tsayar da tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru Elrufa'i don ya gaje a shekarar 2007...

Mafi Shahara