Sunday, April 5, 2026
HomeSiyasaMasu niyyar sauya sheka zuwa jam’iyyar APC a Jihar Enugu ku daina...

Masu niyyar sauya sheka zuwa jam’iyyar APC a Jihar Enugu ku daina tunanin samun tikitin takara kai tsaye -Ministan Tinubu

https://punchng.com/minister-says-no-automatic-ticket-for-apc-defectors/

Ministan kirkire-kirkire, kimiyya da fasaha, Chief Uche Nnaji, ya gargadi masu niyyar sauya sheka zuwa jam’iyyar APC a Jihar Enugu da su daina tunanin samun tikitin takara kai tsaye ko kwace shugabancin jam’iyyar.

Yayin taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a Enugu ranar Asabar, Nnaji ya ce za a karbi masu sauya sheka amma kowa zai bi hanyar zaben fidda gwani. Ya ce wasu ‘yan siyasa da suka rasa matsayi na yawo a Abuja suna shirin shiga APC ta bayan gida domin kwace ikon ta.

Ya kuma yi nuni da rade-radin cewa Gwamna Peter Mbah na iya shiga jam’iyyar, abin da ke tayar da hankalin wasu mambobi, inda ya jaddada cewa babu tikitin kai tsaye ga kowa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata