DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Barayin daji sun yi ajalin askarawan sa kai da gwamnatin jihar Zamfara ta dauka aiki don samar da tsaro

-

A kalla jami’an tsaro 13, ciki har da ‘yan sanda 2 da ‘yan sa-kai 11, sun rasa rayukansu a harin ‘yan bindiga a ƙauyen Adabka, da ke karamar hukumar Bukkuyum, Zamfara.

Shaidu daga kauyukan sun ce maharan sun farmaki ƙauyen a ranar Juma’a da dare, suka yi garkuwa da wasu mazauna yanking sannan suka yi wa jami’an tsaro kwanton ɓauna yayin da suke bin su domin ceto mutanen.

Google search engine

Majalisar dokokin jihar Zamfara ta tabbatar da cewa har yanzu ba a iya ɗaukar gawarwakin ba saboda ‘yan bindigar sun tsaya a dajin da ke kusa.

Rahotanni da jaridar TRT Global ta tattaro sun nuna cewa yankin na fama da hare-haren da ake kaiwa akai-akai duk da yarjejeniyoyin sulhu da gwamnati ta yi da ‘yan bindigar, amma suna karya su suna ci gaba da kai hare-hare.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara