DCL Hausa Radio
Kaitsaye

’Yan Najeriya sun yi kuskure a kayar da gwamnatin Jonathan – Dr. Grema Kyari

-

Ƙungiyar Bring Back Our Goodluck ta bukaci tsohon shugaban ƙasa, Dr. Goodluck Jonathan, da ya sake tsayawa takarar shugaban ƙasa a zaben 2027.

Da yake jawabi a taron manema labarai a Mambayya House da ke Kano, shugaban ƙungiyar, Dr. Grema Kyari, ya ce ’yan Najeriya sun yi kuskure a 2015 wajen kawar da gwamnatin Jonathan ta hanyar ƙuri’a.

Google search engine

Ƙungiyar ta bayyana cewa mulkin Jonathan ya fi samar da kwanciyar hankali da bunƙasar tattalin arziki, inda aka samu farashin kayan abinci da mai a farashi mai sauƙi, tare da shirye-shiryen tallafawa matasa kamar YouWin! da SURE-P.

Kyari ya ce dawowar Jonathan ya zama dole, yana kwatanta shi da dawowar Donald Trump a Amurka da John Mahama a Ghana.

Ya kuma ƙara da cewa, a lokacin Jonathan, buhun shinkafa na sayarwa kusan N7,800, amma a yau ya kai tsakanin N80,000 zuwa N100,000, lamarin da ya jefa miliyoyin ’yan ƙasa cikin yunwa da talauci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara