DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Malam Nasiru El-rufa’i ya jagoranci hadewar jam’iyyar SDP da ADC a Kaduna

-

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya jinjinawa abin da ya kira da hangen nesa bayan da jam’iyyar SDP ta haɗe gaba ɗaya da jam’iyyar ADC a Kaduna.

Lamarin ya faru ne a wata ganawar manyan shugabanni da aka gudanar ranar Asabar, 23 ga Agusta, 2025, a Kaduna, inda El-Rufai ya jagoranci taron.

Google search engine

Taron ya samu halartar manyan ‘yan siyasa daga ADC, shugabannin SDP, tsofaffin kwamishinoni, da wasu daga PDP.

Jaridar Punch ta ruwaito El-Rufai ya ce wannan haɗin gwiwa babban mataki ne wajen samar da ƙarfi guda domin cimma cigaba da shugabanci nagari a jihar.

Shugaban ADC a Arewa maso Yamma, Ja’afar Mohammed Sani, ya yaba da matakin da SDP ta dauka wajen fifita bukatar jama’a a yayin shiga hadakar siyasar ta ADC a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara