Ƙasar Morocco na kan gaba wajen samun tikitin zuwa gasar cin kofin duniya ta 2026, inda ake sa ran za ta zama ta farko daga Afrika da ta samu gurbi a gasar.
Tawagar ƙasar da Achraf Hakimi, ɗan wasan PSG kuma ɗan takara a kyautar zama zakaran dan kwallon duniya “Ballon d’Or ke jagoranta, za ta samu tabbacin gurbi idan ta doke kasar Niger,wannan zai ba ta damar samun maki mai yawa a Group E, muddin Tanzania ba ta yi nasara a kasar Congo Brazzaville a ranar kafin wasan ba.
Morocco na jan ragamar teburi da maki 15 daga wasa 5, yayin da Tanzania ke da maki 9, Zambia da Niger na da 6 kowanne, sai Congo da ba ta samu ko maki guda ba saboda matsalolin gudanarwa.
Idan Morocco ta doke Niger, wasan da za ta buga da Zambia a ranar 8 ga Satumba a Ndola na iya zama na tabbatar da samun tikitin shiga gasar, inda za ta bukaci maki daya kacal.



