DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Morocco na dab da zama kasar Afrika ta farko da ta samu cancantar zuwa gasar cin kofin duniya na 2026

-

Ƙasar Morocco na kan gaba wajen samun tikitin zuwa gasar cin kofin duniya ta 2026, inda ake sa ran za ta zama ta farko daga Afrika da ta samu gurbi a gasar.

Tawagar ƙasar da Achraf Hakimi, ɗan wasan PSG kuma ɗan takara a kyautar zama zakaran dan kwallon duniya “Ballon d’Or ke jagoranta, za ta samu tabbacin gurbi idan ta doke kasar Niger,wannan zai ba ta damar samun maki mai yawa a Group E, muddin Tanzania ba ta yi nasara a kasar Congo Brazzaville a ranar kafin wasan ba.

Google search engine

Morocco na jan ragamar teburi da maki 15 daga wasa 5, yayin da Tanzania ke da maki 9, Zambia da Niger na da 6 kowanne, sai Congo da ba ta samu ko maki guda ba saboda matsalolin gudanarwa.

Idan Morocco ta doke Niger, wasan da za ta buga da Zambia a ranar 8 ga Satumba a Ndola na iya zama na tabbatar da samun tikitin shiga gasar, inda za ta bukaci maki daya kacal.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara