Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa goyon bayansa ga tikitin Musulmi da Musulmi a zaben shugaban kasa na 2023 ba don addini ba ne, illa siyasa ce kawai domin samun nasara.
El-Rufai ya bayyana haka ne a gidan talabijin na Channels ta cikin shirin Sunday Politics, inda ya ce matakin na jam’iyyar APC wani tsari ne na siyasa da aka yi tunani akai domin samun nasara a zabe, ba wai wani abu da ya shafi addini ba.
A cewarsa dama tsarin na siyasa ne, kuma dabarar lashe zabe ce, ba wani batu na addini ba,idan kana neman cin zabe kana duba dukkan dabarun da za su baka nasara.
Ya ce, irin wannan tunani shi ma ya yi lokacin da ya tsaya takarar gwamna a Kaduna a kan tikitin Musulmi da Musulmi, kuma hakan bai tauye wa Kiristoci hakkin su ba,kuma duk shugaban da yake son samun nasara ba zai takaita kansa ga addini ko kabila daya ba dole ne ya nemi mutane ko ta ina ne.



