DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan jihar Neja Umar Bago, ya sauke dukkanin kwamishinoninsa

-

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya sauke dukkanin kwamishinoninsa, tare da umartar manyan sakatarorin ma’aikatun jihar da su ci gaba da rike ragamar ma’aikatun har zuwa lokacin da za a nada sababbin kwamishinoni.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a Litinin din nan yayin taron majalisar zartarwa, inda ya yi gargaɗi ga tsoffin kwamishinonin da kada su yi yunƙurin neman taimako ko shiga sahun masu neman mukaman gwamnati.

Google search engine

Ya ce cikin mako guda zuwa biyu zai sanar da sabuwar majalisar zartarwa, inda ya bayyana cewa ya riga ya yi nazari kan ayyukan kowanne daga cikin tsoffin kwamishinonin.

A cewarsa, akwai wadanda suka taka rawar gani a ayyukansu, yayin da wasu kuma ba su samu damar yin ayyukan da aka dorasu akai ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Jami’ar gwamnatin tarayya da ke Dutse a jihar Jigawa ta kori dalibai 20 tare da dakatar da wasu 15 bisa zarginsu da satar jarrabawa

Jami'ar tarayya da ke jihar Jigawa ta kori dalibai 20 tare da dakatar da wasu 15 daga karatu bisa samunsu da laifin satar jarabawa. Rahotanni sun...

Mafi Shahara