DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tiani na Nijar ya nada Ibrahim Manzo Djallo shugaban hukumar sanya ido kan kafafen yada labarai ta kasa wato ONC

-

A cikin wani kudurin doka ne da ya saka wa hannu shugaban gwamnatin mulkin sojan Nijar Janar ABDOURAHAMANE Tiani ya sanar da nada malan Ibrahim Manzo Djallo shugaban rukunin mujallar Aïr Info da gidan radiyon Sahara a matsayin wanda zai jagoranci hukumar sanya ido kan kafafen yada labarai ta kasar Nijar wato l’ Observatoire National de Communication ONC a takaice.

Daman dai an jima kungiyoyin ‘yan jarida da na ‘yan fafitika a Nijar na kiraye kirayen gwamnatin mulkin sojan kasar da ta girka wannan hukuma domin magance irin matsalolin da ake samu tsakanin gwamnatin da wadansu kafafen yada labaran.

Google search engine

A baya dai tun kafin juyin mulkin ranar 26 ga watan Yulin 2023 akwai makamanciyar wannan hukuma da ake kira Conseil Supérieur de la Communication CSC to amma sojojin suka rusa ta

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara