DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotun Ghana ta yanke wa ’yan Nijeriya uku hukuncin daurin shekaru 96 kan satar motoci

-

Wata kotu a Ghana ta yanke wa wasu ’yan Nijeriya uku hukuncin zaman kurkuku na shekaru 96 kowannen su bisa laifin satar motoci a birnin Kumasi.

An kama mutanen ne a ranar 20 ga Yuni, 2025, bayan an zargesu da satar motocin da aka yi a cikin birnin.

Google search engine

Hukuncin na zuwa ne a daidai lokacin da ake nuna damuwa kan karuwar aikata laifuka da ake zargin baki suna yi a ƙasar.

A watan Yuli dai, hukumar shige da fice ta Ghana ta kama ’yan Nijeriya 50 a Accra bisa zargin damfara ta yanar gizo da kuma fataucin mutane zuwa kasashen waje.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara