DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Trump ya fara mayar ‘yan Nijeriya gida daga Amurka

-

Daily Trust ta ruwaito cewa gwamnatin Amurka a ƙarƙashin shugabancin Donald Trump ta fara mayar da wasu ‘yan Nijeriya gida, a wani sabon shiri da ya kaddamar.

Shugaban kasar Ghana, John Dramani Mahama ne ya bayyana hakan a wata tattaunawa da manema labarai a Accra.

Google search engine

Ya ce mutum 14 ne aka maido daga Amurka, ciki har da ‘yan Nijeriya da wani ɗan Gambia, an sauke su a Ghana, inda daga nan aka tura su ƙasashensu.

Mahama ya ce Ghana ta amince da karɓar ‘yan Afirka ta Yamma da Amurka ke maido wa, kasancewar ba sa buƙatar visa don shiga ƙasar, sai dai ya nuna cewa dangantaka tsakanin Ghana da Amurka ta fara yin sanyi saboda karin haraji da Amurka ta kakaba kan kayayyakin Ghana da kuma takunkumin visa ga ‘yan ƙasar.

A cewar rahoton, Nijeriya ta sha yin watsi da tsarin karɓar ‘yan kasar daga Amurka, tana mai cewa ba za ta lamunci matsin lamba ba.

A baya-bayan nan ma, Amurka ta mayar da wasu mutane zuwa ƙasashe irin su Eswatini, Sudan ta Kudu da Rwanda, abin da kungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam ke kallo a matsayin take haƙƙin waɗanda aka tsare.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara