DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tsoma baki da manyan arewa ke yi wajen tsayar da ɗan takara ci baya ne ga dimukradiyya – Kwankwaso

-

Ɗan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya zargi wasu mutane da yace na ayyana kan su a matsayin jagororin arewa da yin katsalandan a sha’anin zaben dan takarar shugabancin kasa.
A zantawarsa da BBC Hausa, jagoran darikar Kwankwasiyya, ya yi zargin cewa hakan na kawo ci baya ga dimukradiyyar kasar tare da raba kan al’umma har ta kai ga an zabi dan takarar da bai cancanta ba.
Kwankwaso kuma tsohon gwamnan Kano ya jaddada bukatar jagororin su dauki darasi daga abubuwan da suka faru a baya tare da tsame bakinsu a duk wani sha’ani na zaben dan takara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Rashin tabbas da matsalolin tsaro na barazana ga burin ECOWAS na 2050 – Shugaban ECOWAS, Touray

Shugaban kungiyar ECOWAS, Omar Touray, ya ce rashin tabbas a duniya, matsalolin tsaro da matsin tattalin arziki na hana kungiyar cimma burinta na Vision 2050,...

An yi ajalin wata mace mai juna biyu da wani karamin yaro a cikin birnin Kano

Al’ummar Sheka Sabuwar Gandu a karamar hukumar Kano Municipal sun shiga firgici a daren Asabar bayan wasu da ba a san ko su waye ba...

Mafi Shahara