DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamna Zulum ya rage farashin fetur zuwa N600 ga manoman dake yankunan da matsalar tsaro ta shafa

-

Gwamnan jihar Borno Babagana Zulum ya ce gwamnatin jihar za ta rage farashin fetur ga manoma da ke yankunan da matsalar masu tada kayar baya ta shafa.
Zulum ya bayyana hakan ne a jiya Jumu’a, lokacin da yake kaddamar da kayan noma ga manoma 5000 da matsalar tsaro ta raba da gidajensu.
A cewar gwamnan, litar mai da ake saidawa N1,000 zuwa N1,200 a Maiduguri, za a bayar da tallafi don rage farashin ga manoma su rika samu N600, da manufar saukaka musu tsadar kayayyaki da kuma barnar da su ka fuskanta saboda matsalar tsaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3

Wata kotu a Amurka ta yanke wa wani ɗan Najeriya mai zama a San Gabriel Valley, Abiola Femi Quadri, hukuncin ɗaurin shekara 11 da wata...

Natasha ta sake shan alwashin komawa majalisar dattawa a ranar Talata

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, ‘yar Majalisar Dattawa daga jihar Kogi da aka dakatar, ta shigar da ƙara ga Majalisar Dattawa tana neman su girmama hukuncin Babbar...

Mafi Shahara