DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu ya kuduri aniyar magance matsalar rashin aikin yi ga matasa – George Akume

-

Sakataren gwamnatin Najeriya George Akume ya baiyana cewa gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta yi himma wurin magance matsalar rashin aikin yi da inganta rayuwar ‘yan Nijeriya.

Akume, a lokacin da sabbin shugabannin kungiyar matasa ta Nijeriya NYC, ƙarƙashin jagorancin Kwamared Jethro Annum suka kai masa ziyara a Abuja ya jaddada cewa shugaban kasa ya ƙaddamar da manufofi da tsare-tsaren da za su rage radadin rayuwa tare da samar da damar ci gaba ga matasa.

Google search engine

Ya ce gwamnatin su ta na da kyakkyawar alaka da matasa kuma za su ci gaba da tallafawa matasa a dukkan harkoki, ciki har da samar da sakatariyar da ta dace da kayan aiki domin sauƙaƙa wa matasan wajen jagoranci da wayar da kan sauran matasa a fadin Nijeriya saboda su amfana da shirye -shiryen gwamnatin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara