DCL Hausa Radio
Kaitsaye

NiMet ta yi hasashen ruwan sama mai yawa na kwanaki uku a Nijeriya

-

Hukumar kula da yanayi ta Nijeriya NiMet ta bayyana cewa daga ranar Litinin zuwa Laraba za a samu ruwan sama tare da guguwa da tsawa a sassa daban-daban na ƙasar.

An yi gargadin yiwuwar ambaliyar ruwa a wasu jihohin Arewa musamman Adamawa, Taraba da Gombe.

Google search engine

Kazalika za’a samu ruwan sama kadan-kadan a garuruwan da ke yankin kudu a cewar hasashen na hukumar ta kula da yanayi a Najeriya.

NiMet ta shawarci jama’a, musamman direbobi da manoma da su dauki matakan kariya domin kauce wa hadura yayin da ake sa ran ruwan sama mai yawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara