DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojojin saman Najeriya sun lalata maboyar ‘yan bindiga a Borno

-

Rundunar sojin saman Najeriya ta bayyana cewa jerin hare-haren da dakarunta suka kaddamar, ya yi sanadiyyar hallaka ‘yan ta’adda da dama tare da lalata maboyarsu a jihar Borno.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran rundunar Air Commodore Ehimem Ejodame ya fitar a Abuja, kamar yadda jaridar punch ta ruwaito.

Google search engine

Sanarwar ta ce dakarun karkashin shirin Operation Hadin Kai, sun kai farmakin ne a yankunan Bula Madibale da Gezuwa da ke jihar.

Kazalika ya ce an kaddamar da hare-haren ne bayan samun bayanan sirri na taruwar ‘yan ta’addan a yankunan daga sassa daban daban.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara