Rundunar sojin saman Najeriya ta bayyana cewa jerin hare-haren da dakarunta suka kaddamar, ya yi sanadiyyar hallaka ‘yan ta’adda da dama tare da lalata maboyarsu a jihar Borno.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran rundunar Air Commodore Ehimem Ejodame ya fitar a Abuja, kamar yadda jaridar punch ta ruwaito.
Sanarwar ta ce dakarun karkashin shirin Operation Hadin Kai, sun kai farmakin ne a yankunan Bula Madibale da Gezuwa da ke jihar.
Kazalika ya ce an kaddamar da hare-haren ne bayan samun bayanan sirri na taruwar ‘yan ta’addan a yankunan daga sassa daban daban.



