DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta dage sauraron shari’ar Farfesa Usman Yusuf zuwa 19 ga watan Nuwamba

-

Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dage sauraron shari’ar tsohon shugaban hukumar inshorar lafiya ta ƙasa (NHIA), Farfesa Usman Yusuf, zuwa ranakun 19 da 20 ga watan Nuwamba, domin cigaba da shari’a kan tuhumar da ake yi masa da cin hanci da rashawa.

Mai shari’a Chinyere Nwecheonwu ta ɗage zaman ne bayan kammala tambayoyin ga shaida na farko daga bangaren masu shigar da ƙara.

Google search engine

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa tun da farko, shaidar wanda shi ne tsohon darakta a NHIA, Attahiru Ibrahim, ya amince cewa shi ne ya rubuta ƙorafi zuwa hukumar EFCC akan Yusuf a lokacin da yake shugabancin NHIA. Amma rashin lafiyar da ya samu ya sa ba a cigaba da shari’ar a jiya ba.

Hukumar EFCC ta gurfanar da Yusuf a kan tuhuma biyar da suka shafi: karkatar da kudade, amfanar da kansa ta hanyar amincewa da siyan mota, yayin da Farfesa Yusuf din ya ƙi amincewa da laifukan da ake tuhumar sa da su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Jami’ar gwamnatin tarayya da ke Dutse a jihar Jigawa ta kori dalibai 20 tare da dakatar da wasu 15 bisa zarginsu da satar jarrabawa

Jami'ar tarayya da ke jihar Jigawa ta kori dalibai 20 tare da dakatar da wasu 15 daga karatu bisa samunsu da laifin satar jarabawa. Rahotanni sun...

Mafi Shahara