DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu ba shi da niyyar ci gaba da mulki bayan 2031 – Martanin fadar shugaban Nijeriya ga El-rufa’i

-

Fadar shugaban Nijeriya ta tabbatar da cewa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ba shi da wani shiri na zarcewa kan mulki bayan 2031 idan ya sake lashe zaben 2027, tana mai jaddada cewa shugaban kasa na tsayawa tsayin daka kan bin ka’idojin dimokuraɗiyya.

Wannan na zuwa ne biyo bayan wan furuci da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, wanda ya zargi gwamnatin Tinubu da yin kama karya, tare da kwatanta shi da shugaba Paul Biya na Kamaru wanda ya ke mulki tun daga 1982.

Google search engine

Sai dai a martaninsa, mai ba shugaban kasa shawara na musamman, Bayo Onanuga, ya bayyana furucin El-Rufai a matsayin zargi maras tushe da kuma abin dariya.

Ya ce shugaba Tinubu yana girmama dimokuraɗiyya kuma ba shi da niyyar ci gaba da mulki bayan karewar wa’adinsa na biyu a karshen Mayun shekarar 2031.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara