DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Ƴan sandan Neja sun kama mutane 12 kan zargin satar Naira biliyan 4.8 a Kainji

-

Rundunar ƴan sandan jihar Neja ta kama mutane 12 kan zargin sacewa tare da lalata kayan da kimarsu ta kai Naira biliyan 4.8 a tashar wutar lantarki ta Kainji.

Haka kuma ta samu nasarar cafke wasu mutum biyu kan zargin shirya karbar kudaden fansa har Naira miliyan 7.

Google search engine

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Neja SP Wasiu Abiodun ya fitar, ya ce lamarin ya samo asali ne bayan da wani kamfani ya shigar da kara kan zargin wani jami’in tsaro da ke aiki a tashar wutar lantarkin.

A cewar sa, tun da jimawa wadanda ake zargi suka fara shirin gudanar da satar.

Sanarwar ta ce an aikata laifukan ne a lokuta mabambanta, kuma ana ci gaba da gudanar da cikakken bincike kafin gurfanar da wadanda ake tuhuma a gaban shari’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara