Gwamnatin Najeriya ta ware kusan Naira biliyan 200 domin aikin samar da jiragen kasa masu zirga-zirga a cikin biranen Kano da Kaduna.
Ministan yada labarai da wayar da kai Alhaji Mohammed Idris ne ya bayyana haka, yayin wani taron manema labarai a Abuja.
A cewar ministan, gwamnatin shugaba Tinubu ta mayar da hankali wajen ganin ta samar da ayyukan ci-gaba a dukkanin matakai, kamar yadda jaridar punch ta ruwaito.
Haka kuma ya ce gwamnatin na kokarin ganin ba a bar kowane bangare a baya wajen samun muhimman ayyukan ci-gaba ba.



