Jam’iyyar PDP ta ce akwai wadanda suka cancanci tsaya mata takarar shugabancin Nijeriya a zaben 2027, baya ga tsohon shugaban kasar Goodluck Jonathan.
Sakataren jam’iyyar na kasa Debo Ologunaba ne ya bayyana haka, yana mai cewa PDP tana da gwamnoni da kuma wasu manyan ‘yan siyasa da suke da gogewar da za su iya tsaya mata takarar shugabancin Ć™asar a zaben 2027 da ke tafe kasa da shekaru biyu, kamar yadda The Nation ta ruwaito.
Haka kuma, ya ce babu wanda zai hana su gudanar da babban taron jam’iyya a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamba, wanda aka shirya gabatarwa a jihar Oyo.



