DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Matsin rayuwar da ake ciki na shafar lafiyar kwakwalwar ‘yan Nijeriya, in ji Peter Obi

-

Tsohon dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a zaben 2023, Peter Obi, ya bayyana cewa matsin rayuwa da ake fama da shi a yanzu ya fara shafar lafiyar kwakwalwar ‘yan Nijeriya.

Obi, ya bayyana haka ne a shafinsa na X yayin bikin ranar ranar lafiyar kwakwalwa ta duniya a ranar 10 ga Oktoba.

Google search engine

Ya ce talauci, rashin aikin yi da tsadar rayuwa sun sanya wasu matasa shiga cikin damuwa da aikata laifuka.

A cewarsa, rahoton hukumar lafiya ta duniya WHO ya nuna cewa sama da mutane miliyan 40 a Nijeriya na fama da matsalolin lafiyar kwakwalwa, amma ƙasa da likitocin kwakwalwa 300 ne kawai ke kula da su,wannan na nuna yadda ƙasar ke nuna halin ko in kula da fannin lafiya.

Obi ya bukaci gwamnati da ta ɗauki mataki kan wannan batun na kiwon lafiya, tare da buƙatar ƙara yawan likitocin kwakwalwa da kuma samar da asibitocin kwakwalwa a kowane yanki na ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Bola Ahmad Tinubu ya yi ganawar sirri da sabbin hafsoshin tsaro a Abuja

Taron, wanda ya gudana kwanaki uku bayan sanar da sabbin nade-naden, shi ne karo na farko da shugaban kasa ya gana da manyan hafsoshin rundunonin...

Paul Biya ya yi wa masu zanga-zangar sakamakon zabe shagube a Kamaru

Shugaban ƙasar Kamaru, Paul Biya, ya yi shagube ga rikicin siyasar da ke faruwa bayan ayyana shi a matsayin wanda ya lashe sakamakon zaɓen shugaban...

Mafi Shahara