DCL Hausa Radio
Kaitsaye

ASUU ba ta da hujjar shiga yajin aiki domin mun biya dukkanin bukatunta – Gwamnatin Nijeriya

-

Gwamnatin tarayya ta roƙi kungiyar malaman jami’o’i ta ASUU da ta dakatar da yajin aikin da ta fara, tana mai cewa ta cika dukkan bukatun da kungiyar ta gabatar kuma ta mika mata sabon tayin yarjejeniya.

Ministan Ilimi, Tunji Alausa, ya bayyana hakan ne a hirar da aka yi da shi a tashar Channels TV a ranar Litinin, inda ya ce gwamnati ta tattauna da ASUU sau da dama tun bayan karɓar mukaminsa, don haka babu hujjar ci gaba da yajin aiki.

Google search engine

Alausa ya ce, sun biya dukkan bukatun ASUU ɗaya bayan ɗaya, ba dalilin yajin aikin nan don haka muna roƙonsu da su koma makaranta kamar yadda Punch ta ruwaito.

Sai dai a ranar Lahadi ASUU ta sanar da fara yajin aikin gargadi na makonni biyu a dukkan jami’o’in gwamnati, tana mai zargin gwamnatin tarayya da kin cika alkawuran da ta dauka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara