DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Fitar Pantami daga APC ba karamar asara ba ce ga jam’iyyar a Arewacin Nijeriya

-

Jigo a jam’iyyar APC daga Jihar Bauchi, Khamis Darazo, ya bayyana cewa ficewar tsohon ministan sadarwa da tattalin arzikin zamani, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, daga jam’iyyar zai kasance babban rashi ga APC musamman a Arewacin Nijeriya.

Darazo ya bayyana haka ne a ranar Lahadi yayin da yake zantawa da manema labarai a Bauchi, inda ya bukaci fadar shugaban kasa da shugabancin jam’iyyar su gaggauta shawo kan lamarin.

Google search engine

A cewarsa, rahotannin da ke cewa Pantami na shirin barin jam’iyyar suna kara tada hankalin magoya baya, yana mai gargadin cewa hakan zai zama babban koma baya ga jam’iyyar a Arewa da ma kasa baki daya.

Punch ta ruwaito cewa, Darazo ya bayyana Pantami a matsayin mutum mai hangen nesa da kwarewa wanda ya sadaukar da kansa wajen yada ilimi, imani da gaskiya wajen inganta mulki da kuma karfafa matasa a fadin Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara