DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Duk da kiran da gwamnan Kano ya yi na a cire ni, har yanzu akwai kyakkyawar alaka tsakanina da shi – Kwamaishinan ‘yan sandan Kano

-

Kwamishinan ‘yan sanda na Jihar Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ya bayyana cewa duk da kira da Gwamna jihar, Abba Kabir Yusuf ya yi ga Shugaba Bola Tinubu da ya sauke shi daga mukaminsa, har yanzu alaƙarsa da gwamnan tana da kyau tare da mayar da hankali kan tabbatar da zaman lafiya a jihar.

Daily Trust ta ruwaito cewa Abba ya yi wannan kira ne yayin bikin cikar Nijeriya shekara 65 da samun ‘yancin kai, inda ya koka kan rashin halartar kwamishinan a wajen taron da kuma janye jami’an ‘yan sanda daga dandalin bikin.

Google search engine

A yayin taron manema labarai a ofishin rundunar ‘yan sanda, CP Bakori ya ce bangarorinsu biyu na aiwatar da nauyin da kundin tsarin mulki ya dora musu, yana mai cewa babu wata matsala tsakaninsa da gwamnan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara