DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mutane 7 sun hadu da ajalinsu sakamakon harsaniya tsakanin ‘yan bindiga da masu hakar ma’adanai a Birnin Gwari jihar Kaduna

-

Akalla mutane bakwai ne suka rasa rayukansu bayan hatsaniya ya barke tsakanin wasu da ake zargin ’yan bindiga da masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a kauyen Kuyello da ke karamar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna, a ranar Alhamis.

Lamarin da ya faru da misalin ƙarfe 11 na safe ya jefa al’ummar yankin cikin tashin hankali, inda aka ji karar harbe-harbe da suka tilasta mazauna yankin tserewa cikin daji domin tsira da rayukansu.

Google search engine

Rahotannin jaridar Punch sun bayyana cewa rikicin ya faru ne bayan wani da ake zargin dan bindiga ya nemi haraji daga masu hakar ma’adanai, amma suka ƙi biya, lamarin da ya haifar da saɓani har ta kai ga kashe shi.

Bayan faruwar hakan, wasu daga cikin abokan aikinsa suka dawo tsakiyar rana suna harbin kan-mai-uwa-da-wabi, inda suka kashe mutane da dama ciki har da wasu daga cikin masu hakar ma’adinai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara