DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sau 22 ana yunkurin lalata mana matatar mai – Matatar man fetur ta Dangote

-

Kamfanin matatar mai ta Dangote ya bayyana cewa tun bayan da matatar man da ke fitar da ganga 650,000 a rana ta fara aiki, aƙalla sau 22 aka yi yunƙurin lalata kayayyakin aiki ko hana ta gudanar da ayyukanta yadda ya kamata.

Mataimakin shugaban kamfanin mai kula da sashen mai da iskar gas, Devakumar Edwin ne ya bayyana hakan a yayin da tsohon mai taimakawa shugaban ƙasa Reno Omokri ya kai ziyarar gani da ido zuwa matatar da ke Lekki, a jihar Legas.

Google search engine

Edwin ya ce duk waɗannan hare-haren an shawo kansu cikin nasara saboda tsarin tsaro na zamani da matatar ke amfani da shi.

Rahotannin da Daily Trust ta ruwaito sun nuna cewa, matatar ta fuskanci sauye-sauyen ma’aikata da suka shafi kusan mutum 800, wanda hakan ya janyo yajin aiki daga kungiyar manyan ma’aikatan mai da iskar gas ta PENGASSAN, kafin gwamnati ta shiga tsakani aka dakatar da yajin aikin.

Edwin ya kuma karyata jita-jitar da ke cewa matatar tana fama da matsalolin aiki ko na samun danyen mai, yana mai cewa wadannan bayanai ba gaskiya ba ne, illa wani yunƙuri na ɓata suna da nasarorin da kamfanin ke samu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An gudanar da addu’o’in neman tsari daga hare-haren ‘yan bindiga a jihar Neja

Mazauna yankin jihar Neja ta Arewa sun gudanar da addu’o’i na musamman a filin Idi da ke Kontagora, hedkwatar karamar hukumar Kontagora, domin neman taimakon...

‘Yan siyasa a Nijeriya sun fi maida hanakali kan siyasa maimakon magance matsalolin al’umma – Sarkin Onitsha

Sarkin Onitsha, Igwe Nnaemeka Achebe, ya caccaki ‘yan siyasa bisa mayar da hankali kan siyasa maimakon gudanar da mulki yadda ya kamata tun kafin zaben...

Mafi Shahara