DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kaso 95 cikin 100 na jihar Kaduna ‘yan APC ne – Uba Sani

-

Jam’iyyar APC a jihar Kaduna ta karɓi sabbin mambobi, ciki har da ’yan majalisar wakilai guda biyar da kuma ’yan majalisar dokokin jihar Kaduna huɗu tare da dubban magoya baya.

Wani babban gangami da aka gudanar a ranar Asabar ya sa APC yanzu tana da ’yan majalisar wakilai 13 a jihar ta Kaduna yayin da PDP ta rage da uku.

Google search engine

Haka kuma a majalisar dokokin jihar APC tana da mambobi 26 yayin da PDP ke da guda 8.

Taron, wanda aka gudanar a filin wasa na Murtala Square da ke Kaduna, ya samu halartar shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, kakakin majalisar wakilai Tajudeen Abbas, Ministan muhalli Balarabe Abbas Lawal da shugaban hukumar ci-gaban Arewa maso Yamma Lawal Samaila Yakawada tare da dubban magoya bayan jam’iyyar.

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani, yayin da yake jawabi, ya tabbatar wa sabbin shiga cewa APC jam’iyya ce ta haɗin kai wadda ba ta nuna bambanci tsakanin sabbi da tsofaffin mambobinta, yana mai cewa duk wanda ya shigo jam’iyyar APC a yau da waɗanda suka dade a ciki suna da dama iri guda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaba Tinubu ta soki Atiku kan kwatanta gwamnatinsa da ta mulkin soja

Fadar Shugaban Nijeriya ta caccaki madugun adawa Atiku Abubakar, bisa kwatanta gwamnatin Tinubu da mulkin soja, tana mai bayyana kalaman nasa a matsayin abinda basu...

Majalisar Dattawa ta dakatar da muhawara kan gyaran dokar zabe tare da shiga zaman sirri

Majalisar Dattawan Nijeriya ta dakatar da muhawarar kan kudirin dokar zaɓe ta 2022, domin bai wa ’yan majalisa damar yin nazari mai zurfi kafin ɗaukar...

Mafi Shahara