DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kaso 95 cikin 100 na jihar Kaduna ‘yan APC ne – Uba Sani

-

Jam’iyyar APC a jihar Kaduna ta karɓi sabbin mambobi, ciki har da ’yan majalisar wakilai guda biyar da kuma ’yan majalisar dokokin jihar Kaduna huɗu tare da dubban magoya baya.

Wani babban gangami da aka gudanar a ranar Asabar ya sa APC yanzu tana da ’yan majalisar wakilai 13 a jihar ta Kaduna yayin da PDP ta rage da uku.

Google search engine

Haka kuma a majalisar dokokin jihar APC tana da mambobi 26 yayin da PDP ke da guda 8.

Taron, wanda aka gudanar a filin wasa na Murtala Square da ke Kaduna, ya samu halartar shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, kakakin majalisar wakilai Tajudeen Abbas, Ministan muhalli Balarabe Abbas Lawal da shugaban hukumar ci-gaban Arewa maso Yamma Lawal Samaila Yakawada tare da dubban magoya bayan jam’iyyar.

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani, yayin da yake jawabi, ya tabbatar wa sabbin shiga cewa APC jam’iyya ce ta haɗin kai wadda ba ta nuna bambanci tsakanin sabbi da tsofaffin mambobinta, yana mai cewa duk wanda ya shigo jam’iyyar APC a yau da waɗanda suka dade a ciki suna da dama iri guda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara