DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sauya sheka cin amanar al’umma ne – Sanata daga jihar Katsina

-

Sanata Muntari Dandutse mai wakiltar Katsina ta Kudu a jam’iyyar APC ya bayyana sauya sheka daga jam’iyya zuwa wata a matsayin cin amanar jama’ar da suka ba da kuri’unsu.

Yayin muhawarar da majalisar dattawa ta yi kan kudirin sauya dokar zaɓe a ranar Laraba, Dandutse ya ce ya zama dole a samar da doka mai tsauri da za ta takaita yin hakan, inda ya ce ba za ka iya lashe zaɓe a jam’iyya guda sannan ka canza sheka ba tare da doka mai tsauri ba, domin hakan na tauye amanar da jama’a suka ba ka.

Google search engine

Sanatan ya ƙara da cewa duk wani gyara da za a yi wa dokar zaɓe dole ne ta mayar da hankali wajen dawo da amincewar jama’a ga tsarin dimokuraɗiyya da tabbatar da mutuncin zaɓe a ƙasar.

Jaridar Daily Trust ta wallafa cewa, Dandutse ya kuma jaddada bukatar gudanar da dukkan zaɓe a rana ɗaya da bai wa hukumar zaɓe ta INEC ikon gudanar da zaɓukan ƙananan hukumomi domin inganta tsarin mulki.

Sanatan shi ne ɗan majalisar farko daga jam’iyyar mai mulki da ya fito fili ya soki sauye-sauyen jam’iyya da ‘yan majalisun ke yi zuwa cikin jam’iyya mai mulki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Sabon shugaban hukumar zaben ya yi alwashin dawo da ingantacce da sahihin zabe a Nijeriya

Sabon shugaban hukumar zaɓen Nijeriya, INEC, Farfesa Joash Amupitan, SAN, ya sha alwashin dawo da sahihanci da amincewar jama’a ga tsarin zaɓe na ƙasar, yana...

Ba ni ke tsoma baki a gwamnatin Kano ko raba kwangiloli ba – Rabi’u Musa Kwankwaso

Jagoran jam’iyyar NNPP kuma tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya karyata zargin da ake yi masa na tsoma baki a harkokin mulkin...

Mafi Shahara