DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Lakurawa sun yi ajalin makiyaya goma a jihar Kebbi

-

Aƙalla makiyaya goma ne aka ruwaito sun rasu a harin ramuwar gayya da aka kai wa Fulanin kauyen Tilli da ke Ƙaramar Hukumar Bunza ta Jihar Kebbi.

Rahotanni da jaridar Daily Trust ta tattaro sun bayyana cewa bayan ajalin ɗan sa-kain, mutane suka kai hari kan wasu Fulanin yankin, inda aka dauki ran akalla mutane goma a cikin mamayar da aka yi wa sansanoninsu.

Google search engine

Ya ƙara da cewa Shugaban ƙungiyar makiyaya ta Miyetti Allah na kasa (MACBAN) tare da Mataimakin Gwamnan Jihar Kebbi, Sanata Umar Tafida, sun ziyarci yankin domin jajanta wa iyalan waɗanda suka rasa rayukansu a harin.

Da aka tuntubi Jami’in hulɗa da jama’a na Rundunar ‘Yan Sandan Jihar, CSP Nafiu Abubakar, ya ce bai samu labarin faruwar lamarin ba tukuna.

Sai dai ya yi alkawarin binciko gaskiyar lamarin da dawo da bayani, amma bai yi hakan ba har zuwa lokacin kammala wannan rahoto.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara