DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojojin Nijeriya za su murƙushe ‘yan ta’addan Lakurawa — Babban hafsan sojin kasa Janar Waidi Shaibu

-

Babban hafsan sojin kasa, Manjo Janar Waidi Shaibu, ya sha alwashin murƙushe sabuwar ƙungiyar ‘yan ta’addan Lakurawa wadda ke addabar wasu sassan arewacin Nijeriya.

Janar Shaibu, wanda Shugaba Tinubu ya nada kwanan nan, ya bayyana haka ne yayin da Majalisar Dattawa ke tantance shi a Larabar nan.

Google search engine

A cewar sabon hafsan sojin, yana da gogewa a fagen yaki da ta’addanci tun lokacin da ya jagoranci sojoji a jihar Borno, inda ya ce a lokacin sunci karfin Boko Haram, kuma da dama daga cikinsu sun miƙa wuya.

Ya kara da cewa, sun yi amfani da fasahar zamani wajen inganta ayyukan soji, wanda hakan ya taimaka wajen lalata ƙungiyoyin ta’addanci da dama.

Janar Shaibu ya kuma bayyana cewa nan gaba, rundunar soji za ta mayar da hankali wajen ci gaban ma’aikata da kula da jin daɗinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara