DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Muna so a ba mu damar kafa karin kananan hukumomi – Gwamnatin Bauchi

-

Gwamnatin jihar Bauchi ta mika bukatar neman a bata damar kirkirar sabbin kananan hukumomi 29 a jihar.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa mataimakin magatakardar Majalisar Dokokin jihar Bauchi, Musa Yerima, ne ya aika da bukatar neman sahalewar kwamitin gyaran kundin tsarin mulki na kasa domin amincewa.

Google search engine

A halin yanzu, Bauchi na da kananan hukumomi 20 da kundin tsarin mulki na 1999 ya amince da su,idan aka ƙara waɗannan sabbin guda 29 da ake nema, yawan kananan hukumomin jihar zai kai 49,wadda ke da kusan al’umma miliyan 10.

A cikin wasikar da Yerima ya aika wa shugaban kwamitin Majalisar Dattawa kan gyaran kundin tsarin mulki, Sanata Barau Jibrin, ya bayyana cewa suna neman sabbin kananan hukumomin ne bisa tanadin Sashe na 100, sakin layi na 3 na kundin tsarin mulki, kuma ana neman sahalewar Majalisun kasar ta amince da su bisa Sashe na 8(5).

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsare-tsaren Tinubu na farfaɗo da martabar Nijeriya a duniya -Kashim Shatima

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya ce gyare-gyaren da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa na sake gina martabar Nijeriya a idon duniya tare...

Gwamnatin Nijeriya na shirin dakatar da shigo da kayan tsaro daga waje

Gwamnatin Nijeriya ta yi niyyar kera dukkan makami da ake buƙata a cikin gida nan da shekara biyu zuwa biyar masu zuwa. Minista a ma'aikatar Tsaron...

Mafi Shahara