DCL Hausa Radio
Kaitsaye

PDP Bangaren Wike ya dakatar da Damagum yayin da sabon rikicin shugabanci ya sake kunno kai a jam’iyyar

-

Jam’iyyar PDP ta sake fadawa cikin rikici yayin da sabuwar rarrabuwar kai ta kunno kai a cikin shugabancinta, inda wani bangare mai goyon bayan ministan Abuja, Nyesom Wike, ya sanar da dakatar da mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, Umar Damagum, da wasu mambobin kwamitin gudanarwa guda biyar.

Da yake jawabi ga manema labarai a Abuja a ranar Asabar a madadin bangaren, sakataren jam’iyyar na kasa, Sanata Samuel Anyanwu, ya bayyana mataimakin shugaban jam’iyyar na yankin Arewa ta Tsakiya, Mohammed Abdulrahman, a matsayin sabon mukaddashin shugaban jam’iyyar.

Google search engine

Anyanwu ya ce an dakatar da Damagum bisa rashin iya aiki, almundahana, da kin bin hukuncin kotu, tare da tura shi gaban kwamitin ladabtarwa na jam’iyyar.

Haka kuma ya kara da cewa an dakatar da mai magana da yawun jam’iyyar, Debo Ologunagba, bisa fitar da sanarwa ba tare da izini ba, sai mataimakin shugaban jam’iyyar na yankin kudu, Taofeek Arapaja, da kuma mai kula da harkokin kudi, Daniel Woyenguikoro, bisa zargin almundahana.

Hakazalika, an dakatar da shugaban matasa na kasa, Sulaiman Kadade, da mataimakin sakataren kasa, Setonji Koshoedo, na tsawon kwanaki 30 kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Sai dai a baya, kwamitin karkashin jagorancin Damagum shi ma ya dakatar da Sanata Samuel Anyanwu, lauyan jam’iyyar, Kamaldeen Ajibade (SAN), da wasu mambobi biyu, abin da ya kara tsananta rikicin cikin gida da jam’iyyar ke ciki a halin yanzu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar dattawan Nijeriya za ta tattauna da shugaba Tinubu kan kalaman Trump

Majalisar dattawan Nijeriya ta bayyana cewa za ta gana da shugaba Tinubu da bangaren zartarwa domin tattauna batun rikicin diflomasiyya da kalaman shugaban Amurka Donald...

ECOWAS ta yi watsi da zargin Trump na halaka mabiya addinin kirista a Nijeriya

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS ta fitar da sanarwa mai dauke da watsi kan zargin cewa hare-haren ta’addanci da ke ƙaruwa a...

Mafi Shahara