DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam’iyyar SDP ta jaddada dakatarwar da ta yi ma El-Rufai na tsawon shekaru 30

-

Kungiyar shugabannin jam’iyyar SDP na jihohi 37 ta tabbatar da cewa tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, har yanzu yana cikin dakatarwa daga jam’iyyar na tsawon shekaru 30.

Wannan sanarwa ta fito ne bayan jita-jitar da ke yawo cewa El-Rufai na shirin komawa cikin jam’iyyar kafin babban taronta na kasa.

Google search engine

Shugaban kungiyar, Femi Olaniyi, ya shaida wa jaridar PUNCH a ranar Lahadi an Abuja cewa, babu komawa baya a kan hukuncin da kwamitin gudanarwa na kasa ya dauka kan El-Rufai.

A cewarsa, El-Rufai ya shiga jam’iyyar ne ta bayan gida kuma tun a ranar 3 ga watan Afrilu, 2025 an bayyana cewa duk wanda ke son shiga jam’iyyar sai ya bi matakin ofishin mazaba da na jiha, amma El-Rufai bai bi wannan hanya ba. Don haka ne kwamitin kasa ya dakatar da shi har na shekaru 30, kuma wannan hukunci ba zai canza ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara