DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Magoya bayan bangaren Wike sun mamaye hedkwatar PDP a Abuja

-

Wasu magoya bayan bangaren sabon mukaddashin shugaban jam’iyyar PDP, Mohammed Abdulrahman, sun mamaye hedkwatar jam’iyyar da ke Wadata Plaza, Abuja, a ranar Litinin suna rera wakokin goyon baya, tare da bukatar bangaren Umar Damagum ya bar ofis nan take.

Rahotanni sun ce rikicin cikin gida na jam’iyyar ya kara kamari bayan dakatar da sakataren jam’iyya, Sanata Samuel Anyanwu, da lauya Kamaldeen Ajibade na tsawon wata guda, abin da ya haifar da kafa sabon bangare karkashin Abdulrahman.

Google search engine

A daya bangaren, magoya bayan ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, sun gudanar da taro a wani wuri daban inda suka sanar da dakatar da Damagum da kwamitinsa.

Jami’an tsaro sun bazu a wurin domin hana tashin hankali yayin da bangarorin biyu ke kokarin kwace ikon ginin jam’iyyar, inda bangaren Abdulrahman ya mamaye ofishin shugaban jam’iyya na kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Yawan malaman kula da lafiya ‘yan Nijeriya da ke aiki a Ingila ya kai 16,00 – Rahoton Jaridar Punch

Akalla ma’aikatan jinya da ungozoma 16,156 ‘yan Nijeriya sun samu lasisin aiki a kasar Birtaniya tsakanin 2017 zuwa 30 ga Satumba, 2025, a cewar bayanan...

Cin hanci da rashawa na boye irin albarkar da Allah Ya ajiye a Nijeriya in ji shugaban hukumar EFCC

Shugaban Hukumar EFCC, Ola Olukoyede, ya ce cin hanci da rashawa na boye albarkar da Allah Ya yi wa Nijeriya tare da hana ƙasar cimma...

Mafi Shahara