DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba a take hakkin Kiristoci a Nijeriya ba – Babban hafsan tsaron Nijeriya

-

Babban hafsan tsaron Nijeriya Janar Olufemi Oluyede ya karyata ikirarin cewa ana zaluntar Kiristoci a Nijeriya, inda ya ce babbar matsalar Nijeriya ita ce ta’addanci.

Janar Oluyede ya bayyana hakan ne yayin zantawa da manema labarai a Abuja a ranar Litinin lokacin da ya mayar da martani kan kalaman shugaban Amurka Donald Trump wanda ya zargim ‘yan ta’adda na kai hare-hare kan Kiristoci.

Google search engine

Oluyede ya ce sojojin Nijeriya na aiki tuƙuru wajen yaƙar ta’addanci da tabbatar da tsaro, tare da samun nasara sakamakon sabon tsarin tsaro da shugaba Tinubu ya kafa.

Hakazalika ya ƙara da cewa rundunar soji za ta cigaba da ƙoƙari wajen dawo da zaman lafiya tare da buƙatar haɗin kan ƙasashen duniya domin yaƙi da ta’addanci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar dattawan Nijeriya za ta tattauna da shugaba Tinubu kan kalaman Trump

Majalisar dattawan Nijeriya ta bayyana cewa za ta gana da shugaba Tinubu da bangaren zartarwa domin tattauna batun rikicin diflomasiyya da kalaman shugaban Amurka Donald...

ECOWAS ta yi watsi da zargin Trump na halaka mabiya addinin kirista a Nijeriya

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS ta fitar da sanarwa mai dauke da watsi kan zargin cewa hare-haren ta’addanci da ke ƙaruwa a...

Mafi Shahara