DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar dokokin Amurka na neman haramta biza da toshe dukiyar mambobin Miyetti Allah

-

Sabon kudiri da majalisar dokokin Amurka ke tattaunawa ya bukaci kakaba takunkumin biza da kulle dukiyar mambobin kungiyoyin Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) da Miyetti Allah Kautal Hore, bisa zargin take hakkin ‘yancin addini a Nijeriya.

Kudirin, wanda dan majalisar Amurka Christopher Smith ya gabatar a ranar Talata, ya zo ne bayan shugaban kasa Donald Trump ya ayyana Nijeriya a matsayin ƙasa mai damuwa ta musamman kan batun kisan Kiristoci, duk da musantawar gwamnatin Nijeriya.

Google search engine

Rahotanni daga The New York Times sun nuna cewa rundunar sojin Amurka ta riga ta tsara shirin kai hare-hare idan lamarin ya dauki zafi. Kudirin ya kuma hada ‘yan Fulani a jihohin Benue da Filato cikin jerin kungiyoyin da ake zargi da take ‘yancin addini.

Idan kudirin ya wuce, Amurka za ta samu damar kakaba takunkumin biza da kulle kadarorin duk wanda aka samu da hannu a irin wadannan ayyuka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Akwai yiwuwar madugun adawar Kamaru Isa Tchiroma yana Nijeriya ya boye – Rahotanni

Madugun adawar Kamaru, Issa Tchiroma Bakary, wanda ya kalubalanci nasarar Paul Biya, yana iya kasancewa yana a Nijeriya kamar yadda Africa Intelligence ta ce, amma...

Fusatattun matasa sun hallaka limamin masallaci a jihar Kwara bisa zargin maita

Wasu fusatattun matasa a garin Sokupkpan da ke ƙaramar hukumar Edu a jihar Kwara sun hallaka limamin masallacin yankin, Malam Abdullahi Audu, bisa zargin cewa...

Mafi Shahara