DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Akpabio ya gargadi minista a majalisa da ka da ya amsa duk wata tambaya kan kalaman Trump

-

Shugaban majalisar dattawan Nijeriya, Godswill Akpabio, ya gargadi wanda aka zaba domin mukamin minista, Barista Kingsley Udeh (SAN), da kada ya amsa kowace tambaya da ta shafi kalaman shugaban Amurka Donald Trump game da Nijeriya.

Udeh, wanda shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya zaba domin maye gurbin tsohon ministan kimiyya da fasaha, Uche Nnaji, ya bayyana a gaban majalisar a ranar Alhamis don tantancewa.

Google search engine

Nnaji ya yi murabus ne a watan da ya gabata bayan cece-kuce kan sahihancin takardun karatunsa.

Lokacin tantancewar, Akpabio ya bukaci Udeh da ya gabatar da kansa sannan ya ce, tambayar da kawai zan roƙe ka kada ka amsa ita ce wadda ta shafi Trump.

Daga karshe, majalisar ta amince da nadin Udeh a matsayin minista ta hanyar kada kuri’ar murya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Akwai yiwuwar madugun adawar Kamaru Isa Tchiroma yana Nijeriya ya boye – Rahotanni

Madugun adawar Kamaru, Issa Tchiroma Bakary, wanda ya kalubalanci nasarar Paul Biya, yana iya kasancewa yana a Nijeriya kamar yadda Africa Intelligence ta ce, amma...

Fusatattun matasa sun hallaka limamin masallaci a jihar Kwara bisa zargin maita

Wasu fusatattun matasa a garin Sokupkpan da ke ƙaramar hukumar Edu a jihar Kwara sun hallaka limamin masallacin yankin, Malam Abdullahi Audu, bisa zargin cewa...

Mafi Shahara