DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan sanda sun kama dan fashi da makamin da ya boye bindigarsa cikin biredi a Nijeriya

-

Rundunar ‘yan sandan jihar Delta ta kama wani matashi da ake zargin dan fashins, wanda aka gano ya boye da bindiga a cikin Burodi.

Mai magana da yawun rundunar, SP Bright Edafe, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Asabar a garin Asaba, babban birnin jihar.

Google search engine

Edafe ya ce jami’an sun kama wanda ake zargin, Nnamdi Stanley Chibuike mai shekaru 24, lokacin da suke gudanar da binciken ababen hawa a Koka Roundabout, Asaba, ranar 6 ga Nuwamba, 2025, a cewarsa, an gano bindiga kirar gida a cikin Burodi, kuma an kama wanda ake zargi nan take.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Abaniwonda Olufemi, ya jinjinawa jami’an bisa wannan nasara, yana mai cewa hakan na nuna yadda rundunar ke ci gaba da gudanar da ayyukanta cikin kwarewa domin dakile laifuka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara