Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu ya yaba wa shugaban hukumar zabe ta kasa INEC, Farfesa Joash Amupitan, bisa gudanar da abin da sahihin zabe a jihar Anambra a ranar Asabar.
A cewar shugaban kasa, hukumar ta nuna ci gaba wajen gudanar da zabe cikin gaskiya da adalci, inda ya bukaci ta ci gaba da inganta ayyukanta don ƙarfafa tsarin dimokuraɗiyya a Nijeriya.
Hukumar INEC ta bayyana Farfesa Charles Soludo na jam’iyyar APGA, a matsayin wanda ya lashe zaben da kuri’u 422,664.



