DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An garkame mutane sama da 700 bisa laifukan da suka shafi ta’addanci – Gwamnatin Nijeriya

-

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa an yanke wa mutane sama da 700 hukunci saboda laifukan da suka shafi ta’addanci a fadin kasar, yayin da wasu ke ci-gaba da fuskantar shari’o’i a kotuna daban-daban.

Ministan yada labarai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce kotun musamman ta shari’ar ‘yan ta’addan Arewa maso Gabas ta gudanar da zama sau bakwai, inda aka samu sama da mutane 700 da laifuka tare da aikewa da su gidan yari, kuma yanzu tana zaman nata na takwas don sauraron sabbin shari’o’i.

Google search engine

Idris ya kara da cewa hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta kammala bincike kan manyan laifuka kamar harin cocin Owo da Nyanya, yayin da ‘yan sanda da jami’an NSCDC ke ci-gaba da shari’o’i a fadin kasar kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

A cewarsa, babban lauyan gwamnati na jagorantar dukkanin hukumomi wajen tabbatar da adalci cikin lokaci da kuma hukunta masu aikata laifukan ta’addanci har ma da satar albarkatun kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara