DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Injiniya Sagir Koki ya fice daga jam’iyyar NNPP

-

Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar birnin Kano a matakin tarayya Injiniya Sagir Ibrahim Koki, ya bayyana ficewarsa daga NNPP saboda rikicin cikin gida da ke kara kamari a cikin jam’iyyar.

A cikin wata wasika da ya rubuta ranar 11 ga Nuwamba, 2025, wacce ya tura wa shugabar jam’iyyar na mazabar Zaitawa, Koki ya ce ya dauki wannan mataki ne bisa tsarin dokar ƙasa da ke ba kowane ɗan Nijeriya ‘yancin shiga ko barin kowace jam’iyya.

Google search engine

Ya ce rikicin shugabanci da ke addabar jam’iyyar a matakin kasa ya yi tsananin da har ya zama abin da ke hana shi gudanar da aikinsa yadda ya kamata da kuma wakiltar al’ummar Kano Municipal yadda ya kamata.

Hon. Koki, wanda aka zabe shi karkashin jam’iyyar NNPP a 2023, ya gode wa jam’iyyar bisa damar da ta bashi ya yi hidima ga al’umma, yana mai bayyana cewa goyon baya da amincewar da ya samu daga ‘ya’yan jam’iyyar sun kasance abin alfahari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara