DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya jijina ma tawagar Super Eagles ta Nijeriya kuma ya bukaci su mayar da hankali kan gasar cin kofin nahiyar Afrika

-

Shugaba Bola Tinubu ya yaba wa tawagar kwallon kafa ta Nijeriya, Super Eagles bisa jajircewarsu a wasan neman gurbin gasar cin kofin duniya ta 2026, duk da rashin nasarar da suka sha a hannun DR Congo bayan bugun fenariti a Rabat, Morocco.

Wasan ya ƙare 1 da 1 bayan mintuna 120, inda DR Congo ta doke Nijeriya da ci 4 da 3 a bugun fenariti.

Google search engine

Tinubu ya ce dole a jinjina ƙoƙarin ‘yan wasan duk da ba a samu sakamakon da ake so ba, kamar yadda mai ba shi shawara kan labarai, Bayo Onanuga, ya bayyana cewa lokaci ya yi da za a duba kura-kuran da aka samu a wasan, tare da gyara duk wani gibin da ya hana ƙungiyar samun nasara.

A cewarsa, yanzu hankali ya koma kan gasar kofin nahiyar Afrika da za a yi a Morocco daga watan Janairu zuwa Fabrairu 2026 inda ya ce Super Eagles na bukatar dawo da kima da martabarsu a gasar nahiyar.

Tinubu ya kuma bukaci ‘yan Nijeriya su cigaba da mara wa ƙungiyar baya, yana cewa duk da rashin sa’a, Eagles sun nuna jajircewa da himma tun daga wasan farko har zuwa bugun fenaritin da ya yanke hukuncin karawar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara